Mohammed Bassim Rashid ( Larabci: محمد باسم; an haife shi ranar 3 ga watan Yulin shekarar 1995) ƙwararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne wanda ke taka leda a matsayin ɗan wasan tsakiya ga ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Indonesiya Persib Bandung da ƙungiyar ƙasa ta Falasdinu.[1]
Kwallan kafa
A ranar 17 ga Yunin shekarar 2021, Ya rattaba hannu kan kwangilar yarjejeniyar shekara guda tare da kulob din Indonesiya Liga 1 Persib Bandung. [2] Ya buga wasansa na farko na kwararru a kungiyar, a cikin nasara 1-0 da Barito Putera a ranar 4 ga Satumban shekarar 2021.[3]
Cin kwallo
A ranar 11 ga Satumbar shekarar 2021, Rashid ya fara zira kwallo a kulob din tare da zira kwallaye biyu a cikin 2021-22 La Liga 1, inda suka ci Persita Tangerang 2-1.[4]Bassim ya kasance cikin tawagar Falasdinu a gasar cin kofin nahiyar Asiya ta AFC na shekarar 2019 a Hadaddiyar Daular Larabawa.[5]